Yusuf Maitama Tuggar: Daga Diflomasiyya Zuwa Fatan Gina Sabuwar Jihar Bauchi


Muazu Abubakar Albarkawa, Kaduna


Batun zaɓen gwamnan shekarar 2027 a Jihar Bauchi ta dauki sabon salo mai jan hankali da ban sha'awa sakamakon fitowar tsohon Ministan Harkokin Waje, Yusuf Maitama Tuggar, a matsayin dan takara tare da dimbin kwarewa a harkokin diflomasiyya, gogewa a majalisa, da kusanci da al’umma, takararsa na zama wata alama ta fata, sabuwar rayuwa, da shugabanci mai manufa.

An haifi Tuggar a ranar 12 ga Maris, 1967, cikin gida mai alaka da siyasa a Gamawa, inda tun daga farko al’amuran jagoranci suka bayyana a rayuwarsa. Mahaifinsa, Abubakar Tuggar, ya kasance fitaccen dan siyasa a lokacin Jamhuriya ta Farko, wanda ya kafa tubalin hidimar jama’a da ya shafi rayuwar Tuggar. Tun yana karami, ya taso cikin darussan shugabanci, nauyi, da kishin kasa wadanda suka zama ginshikin rayuwarsa.

A bangaren ilimi, Tuggar ya yi fice a matsayin mutum mai zurfin tunani da hangen nesa na duniya. Ya yi karatun hulda da kasashen waje, sannan ya kara ilimi a Jami’ar Bath da kuma digiri na biyu daga Jami’ar Cambridge. Kwarewarsa a bangaren kasuwanci, musamman a matsayin babban jami’in gudanarwa na kamfanin Nordic Oil and Gas Services, ta kara masa basira a harkokin shugabanci da tsare-tsare.

Shigarsa siyasa ta fara ne da wakiltar mazabar Gamawa a Majalisar Wakilai daga 2007 zuwa 2011, inda ya nuna kwarewa sosai. A matsayin Shugaban Kwamitin Kula da Sayen Kayayyakin Gwamnati, ya taka muhimmiyar rawa wajen lura da yadda ake kashe kudaden gwamnati a fannoni kamar mai da gas, ilimi, lafiya, da ruwa. Gudunmawarsa wajen karfafa gaskiya da rikon amana, musamman kafa Majalisar Kula da Sayen Kayayyakin Gwamnati, ta zama abin koyi.

Ya kuma taka rawa a dokokin inganta amfani da kayan cikin gida a bangaren mai da gas, tare da kasancewa cikin kwamitoci da dama ciki har da harkokin waje da korafe-korafen jama’a. Gabatar da kudirin dokar hana zaluncin safarar dabbobi ya nuna yadda yake kula da jin dadin al’umma.

A matakin kasa da kasa, aikinsa a matsayin jakadan Najeriya a kasar Jamus daga 2017 zuwa 2023 ya kara masa kima a matsayin gogaggen diflomas. Ya taka rawa a tarukan duniya kan sauyin yanayi, sannan ya taimaka wajen bunkasa alakar kasashen biyu, ciki har da ziyarar Angela Merkel zuwa Najeriya. Har ila yau, ya jagoranci dawo da kayan tarihi na Benin daga Jamus, abin da ya nuna kishinsa ga al’adu da kwarewarsa a diflomasiyya.

Nadin da aka yi masa a matsayin Ministan Harkokin Waje karkashin shugabancin Bola Ahmed Tinubu a 2023 ya kara tabbatar da amincewar da ake da shi a kansa. Amma murabus dinsa a 2026 domin tsayawa takarar gwamnan Bauchi ya nuna cewa burinsa shi ne hidimar jama’a ba mulki kawai ba.

A yayin bayyana takararsa, Tuggar ya bayyana matsalolin da ke addabar jihar Bauchi, talauci, rashin aikin yi, rashin tsaro, da kuma karancin lafiya da ilimi.

“Jihar mu na tsaka mai wuya,” in ji shi, yana nuna cewa lokaci ya yi da za a kawo sauyi.

Sai dai ba wai ya tsaya kan bayyana matsala ba, ya gabatar da mafita tsare-tsare masu inganci da za su bunkasa noma, wanda shi ne ginshikin tattalin arziki. Tsarinsa ya hada da noma a duk shekara, bunkasa kiwo, da kuma sabunta hanyoyin kiwo domin rage rikici da kara yawan amfanin gona.

“Ba wai alkawari kawai ba ne; muna da tsari,” in ji shi, yana tabbatar da cikakken shirinsa.

Ya kuma yi alkawarin biyan albashi a kan lokaci, inganta kasuwanni, da samar da masana’antun sarrafa kayan gona domin samar da ayyukan yi. Burinsa shi ne fitar da jihar daga talauci zuwa wadata.

A bangaren tsaro, ya gabatar da tsarin tsaron al’umma, tattaunawa, da amfani da sarakunan gargajiya tare da hadin gwiwa da jami’an tsaro.

Abin da ya bambanta Tuggar shi ne hadin gwiwar fahimtar gida da kwarewar duniya. Wannan ya sa yake da damar kawo sauyi mai ma’ana.

Ga al’ummar Bauchi, wannan lokaci wata dama ce ta sake fasalin makoma. Zaben Tuggar na iya zama sabon babi na cigaba, hadin kai, da wadata.

Al’ummar Bauchi an san su da jajircewa da hadin kai. Daga manoma zuwa ‘yan kasuwa, sun nuna karsashi da hakuri duk da kalubale. Amma suna bukatar shugaba da zai mayar da kokarinsu ya zama cigaba.

Zaben Tuggar na ba su dama su hada karfinsu da shugabanci mai hangen nesa domin kawo cigaba mai dorewa.

Wannan ba siyasa kawai ba ce, illa tabbatar da makoma mai haske ga al’umma.


Muazu Abubakar Albarkawa ya rubuto daga Kaduna.

Comments

Popular posts from this blog

Nuhu Bamalli Polytechnic Gets NCCE Approval, Begins Admission into Expanded NCE Programmes

Zazzau Mourns: Eze Ndi Igbo of Zazzau's Burial Brings City to Standstill

KADVS assures residents of safety during Christmas, New Year celebration